Annobar zazzabin denge ta yadu a Burkina Faso
November 24, 2023![Burkina Faso Ouagadougou | Coronavirus Medizinische Versorgung](https://static.dw.com/image/55337941_800.webp)
Talla
Ma'aikatar lafiya ta kasar ta ce kawo yanzu tun farkon shekara mutane 570 suka mutu da zazzabin dengen a Burkina Faso. Don kokarin hana ci gaban cutar, gwamnati ta kaddamar da wani shiri na fesa maganin sauro a garuruwan biyu da abin ya fi shafa Ouagadougou da Bobo-Dioulasso.Burkina Faso na fama da zazzabin Dengue tun a shekarun ta 1960, amma a farkon shekarar ta 2017 da aka tabbatar an samu bullar cutar, inda ta kashe mutane 13.