1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ziyara Jose Manuel Barroso a Sudan

October 2, 2006

Shugaban hukumar zartaswa ta kungiar gamaya turai turai, Jose Manuel Barroso ya kai ziyara gani da ido a ƙasar Sudan.

Barroso da tawagar sa, sun tantana da shugaba Omar El Bashir, a game da halin da ake ciki, a Darfur, da kuma mahimmancin aika dakarun shiga tsakani na Majalisar Dinkin Dunia a wannan yanki.

Saidai Jose Manuel Barroso, bai samu nasara ciwo kan shugaban ƙasar Sudan ba, a game da batun amincewa da karɓar rundunar Majalisar Dinkin Dunia.

Bayan wannan tantanwa Baroso da tawagar sa, sun ziyarci Darfur, yankin da ke fama da tashe tsahen hankulla, a tsawan shekaru 3.

A taron manema labarai da ya kira a birnin Al-fasher na yankin Darfur, Jose manuel Barroso, yayi huruci bayan wannan ziyara.

A ɗaya tawagar, EU ta ziyarci cibiyar ƙungiyar tarayya Afrika, a birnin Addis Ababa, na ƙasar Ethiopia, kuma nan gaba a yau za a gana, tsakanin tawagar ta turai, da shugaban hukumar zartaswa na AU, Alpha Omar Konare.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW