1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ziyarar Merkel a nahiyar Afirka

October 3, 2007

A yau SGJ Angela Merkel ta ke fara rangadin wasu kasashen Afirka kudu da Sahara inda za´a mayar da hankali akan ´yancin bil Adama cutar AIDS ko SIDA, hadin kan tattalin arziki da rikicin siyasa da ake fama da shi a kasar Zimbabwe. Merkel zata fara yada zango ne a Addis Ababa babban birnin kasar Ethiopia wato Habasha. Zata gabatar da jawabi a zauren KTA sannan ta tattauna da shugaban hukumar tarayyar Afirka Alpha Oumar Konare. Taron na matsayin share fage na wani taron koli tsakanin tarayyar Turai da tarayyar Afirka wanda za´a gudana a birnin Lisbon na kasar Portugal a cikin watan desamba. SG ta Jamus zata kuma ziyarci kasashen ATK da Liberia.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW