1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ministar harkokin wajen Jamus tana ziyarar yammacin Afirka

Suleiman Babayo ZMA
April 11, 2022

Ministar harkokin wajen Jamus Annalena Baerbock tana fara ziyarar aiki a kasashen Mali da Jamhuriyar Nijar da ke yankin yammacin Afirka.

Berlin | Außenministerin Annalena Baerbock
Hoto: Michael Sohn/AP/picture alliance

Ministar harkokin wajen Jamus, Annalena Baerbock tana fara ziyarar aiki a kasashen Mali da Jamhuriyar Nijar da ke yankin yammacin Afirka. A birnin Bamakon na Mali Baerbock za ta gana da Assimi Goïta shugaban gwamnatin mulkin soja ta wucin gadi da ministan harkokin wajen kasar Abdoulaye Diop. Sannan ta gana da wakilan Tarayyar Turai kan sojojin Jamus kimanin 300 da ke ba da horo a kasar ta Mali mai fama da tashe-tahsen hankula.

A birnin Yamai fadar gwamnatin Jamhuriyar Nijar, ministar harkokin wajen Jamus, Annalena Baerbock za ta gana da Shugaba Mohamed Bazoum da ministan harkokin wajen kasar Hassoumi Massoudou inda za a tattauna kan batun dakarun Jamus da ke yankin sannan za ta gana da wakilan kungiyoyion fararen hula a duk kasashen biyu. Yankin dai na fama da karin karancin abinci bayan kutsen da Rasha ta kaddamar a kan Ukraine.